Maniyyata bikin Easter sun gamu da ajalinsu a Afrika ta Kudu
Hukumomin yankin Limpopo sun tabbatar da afkuwar lamarin tare da bayyana cewa wani yaro daya 'dan shekara 8 kadai ya tsira da ransa a hadarin da a halin yanzu yake kwance a asibitin lardin.
Maniyyata bikin na Ista sun gamu da ajalinsu ne bayan motan ta fado daga kan wata gada daga bisani ta kone kurmus. Hukumomin yankin sun bayyana cewa motar ta taso ne daga makwabciyar kasar ta Afrka ta Kudu wato Botswana zuwa birnin Moria da ake gudanar da gagarumin bikin ibadar Ista a duk shekara.
Karin bayani: Bikin Easter a halin cutar coronavirus
Ko a bara, mutane sama da 200 suka mutu adai wannan hanyar sakamakon hadarin da ke tattare da hanyar mai kwazazzabai da tsaunuka.