'Yan Sanda a Katsina sun Musanta Kisan Mutane 40, Sun Fadi Adadin da aka Rasa
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Katsina-Rundunar ‘yan sandan Katsina ta musanta labarin cewa 'yan ta'addan da suka kai hari jihar sun kashe mutane 40 a makon da ya gabata.
Rahotanni sun bayyana cewa mutane 40 ne suka mutu a harin da miyagun suka kai unguwar Lamido a karamar hukumar Bakori ta jihar Katsina.
Daily Trust ta tattaro cewa a sanarwar da jami'in hulda da jama'a na rundunar 'yan sandan jihar Katsina, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya fitar, ya tabbatar da harin.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta bayyana cewa wasu ’yan ta’adda dauke da mugayen makamai sun kai hari Unguwar Lamido, kuma sun harbe mutane 11.
Kakakin rundunar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.
Peoples Gazette Nigeria ta wallafa cewa ofishin DPO na babban ofishin ’yan sanda a karamar hukumar Bakori ne ya jagoranci jami’ansa da hadin gwiwar ’yan banga suka kai dauki tare da dakile karuwar barnar.
A baya mun kawo muku rahoton cewa sun yi galaba kan 'yan ta'addar da suka sace 'ya'yan 'dan majalisa a jihar Zamfara, Aminu Ardo.
Dakarun 'yan sanda da hadin gwiwar ofishin mai ba shugaban kasa shawara ne suka samu nasarar kubutar da yaran biyu bayan watanni 17.
Asali: Legit.ng