Home Back

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa da Najeriya da sauran sassan duniya 05/06/2024

bbc.com 2024/10/5

Rahoto kai-tsaye

An fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasa zagaye na biyu a Iran

.

Asalin hoton, AFP

An fara kaɗa kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasar Iran zagaye na biyu, da za a fafata tsakanin mai ra'ayin riƙau, Saeed Jalili da mai ra'ayin kawo sauyi, Masoud Pezeshkian.

An samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri'a a zagayen farko, duk da kiran fitowa zaɓen da jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei ya yi.

Sai daia a wannan karon ma jaogran addainin ya sake nanata kiransa na fitowar masu zaɓe a zaɓen zagaye na biyun.

A makon da ya gabata ne dai aka yi zaɓen zagayen farkon, inda duka 'yan takara suka gaza samun kashi 50 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa.

Zaɓen na zuwa a daidai lokacin da ƙasar ke fama da jerin takunkuman karya tattalin arziki daga ƙasashen Yamma da kuma halin da yankin Gabas ta Tsakiya ke cikin, musamman yaƙin Gaza.

People are also reading