KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa da Najeriya da sauran sassan duniya 05/06/2024
An fara kaɗa kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasar Iran zagaye na biyu, da za a fafata tsakanin mai ra'ayin riƙau, Saeed Jalili da mai ra'ayin kawo sauyi, Masoud Pezeshkian.
An samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri'a a zagayen farko, duk da kiran fitowa zaɓen da jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei ya yi.
Sai daia a wannan karon ma jaogran addainin ya sake nanata kiransa na fitowar masu zaɓe a zaɓen zagaye na biyun.
A makon da ya gabata ne dai aka yi zaɓen zagayen farkon, inda duka 'yan takara suka gaza samun kashi 50 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa.
Zaɓen na zuwa a daidai lokacin da ƙasar ke fama da jerin takunkuman karya tattalin arziki daga ƙasashen Yamma da kuma halin da yankin Gabas ta Tsakiya ke cikin, musamman yaƙin Gaza.