Muna Buƙatar Bishiya 1 Tsakanin Gidaje 5 Domin Yaƙar Ɗumamar Yanayi Inji Anka
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Kano, Najeriya– Ƙungiyar rajin kare muhalli ta ƙasa (Nigerian Environmental Society) ta ce har yanzu duniya ba ta kai gaɓar da za a gaza samun yanayi mai kyau ba. Ɗaya daga ƙusoshin ƙungiyar, Umar Saleh Anka ya shaidawa Legit Hausa cewa idan aka ɗauki matakai cikin hanzari, za a gyara muhalli kuma ɗumamar yanayi da ake fuskanta zai ragu.
A kalamansa:
"Duniya ba ta kai wannan gaɓar da za a ce ta kai yadda ba za a iya dawowa baya ba, duk da cewa muna da yawa."
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tun a farkon shekarar nan ne hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NIMET) ta yi gargadin za a fuskanci matsanancin zafi a wasu johohin Arewa kamar yadda Channels tv ta ruwaito. Jihohin da ta ce na fuskantar barazanar tsananin zafi sun haɗa da Abuja, Kano, Sokoto, da jihar Kogi kamar yadda Premium Times Nigeria ta wallafa.
A cewar mai fafutukar kare Muhalli, Umar Saleh Anka, akwai buƙatar a jerin kowane gida biyar, a samu aƙalla bishiya guda ɗaya. Anka ya ce ana yawan gine-gine, ana yawan hawa babura da sauran abubuwan hawa, kuma duk yawancin gidajen da ake ginawa sababbi ba a dasa bishiyoyi gaskiya a ciki.
Mai fafutukar kare muhallin ya ce akai bambanci sosai tsakanin iskar wurin da ake da bishiya da wurin da babu. "Ya kamata a ce duk gida biyar, akwai bishiya misali guda ɗaya a kusa da ita, a iya ɗaukan ta ma a matsayin bishiyar al'umma."
Hukumar NIMET ta yi gargaɗin za a fuskanci tsananin zafi a jihohin Borno da Yobe yayin bukukuwan sallah ƙarama.
Amma a wasu jihohin kamar Kebbi, tsawa za ayi na kwanaki uku, wato daga Litinin zuwa Laraba.
Asali: Legit.ng