Home Back

Masar za ta dauki nauyin taron sasanta rikicin Sudan

dw.com 2024/7/6
Janar al-Burhan na Sudan da Shugaba al-Sisi na Masar
Shugaba al-Burhan na Sudan da Shugaba al-Sisi na kasar Masar

Babban burin taron da za a yi cikin watan gobe, shi ne samun yarjejeniyar samar da dawwamammen zaman lafiya da zai kawo karshen rikicin da Sudan ta fada a ciki.

Tun cikin watan Afrilun bara ne dai kasar ta Sudan ta fada yakin basasa, sakamakon takaddamar siyasa tsakanin sojojin kasar karkashen Shugaba Abdul Fattah al-Burhan da tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdan Dagalo.

Dubban fararen hula ne dai aka yi kiyasin sun salwanta kawo i yanzu a kasar.

Muhimman kasashe Irin su Amurka da Masar da ma Saudiyya, sun yi ta kokarin samar da masalaha kan rikicin na Sudan amma lamarin ya ci tura.

People are also reading