Albashi: Daga Karshe Shugaba Tinubu Ya Fadi Abin da Gwamnati Za Ta Biya Ma'aikata
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ce gwamnatinsa za ta amince ne kawai da sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata na ƙasa wanda za ta iya biya.
Tinubu ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen liyafar cin abincin dare na bikin ranar dimokradiyya a ranar Laraba 12 ga watan Yuni.
Shugaban ƙasan ya ce zai sanar da Godswill Akpabio da mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin idan ya sauya ra’ayi kan shawarar biyan N62,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi, cewar rahoton jaridar Vanguard.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamnatin tarayya/gwamnatocin jihohi da kuma ƙungiyoyin kamfanoni masu zaman kansu (OPS) ne suka amince da biyan N62,000.
Jaridar The Nation ta ce, an miƙa shawarar ga sakataren gwamnatin tarayya, George Akume yayin da ake sa ran Tinubu zai aika da abin da ya amince da shi a matsayin ƙudiri ga majalisar tarayya.
"Shugaban majalisar dattawa, mataimakin shugaban majalisar dattawa, za ku sami sanarwa idan na canza shawara kan mafi ƙarancin albashi."
"Za mu yi, abin da Najeriya za ta iya, abin da za ku iya, abin da zan iya. Ana cewa ka tsaya daidai matsayinka, kada ka ƙure kanka."
- Bola Ahmed Tinubu
A wani labarin kuma, kun ji cewa ƙungiyar kwadago ta ƙasa (NLC) ta musanta iƙirarin shugaban ƙasa Bola Tinubu na cewa an cimma matsaya kan sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata na ƙasa.
Ƙungiyar ta dage cewa har yanzu tana kan buƙatar ta na neman a biya N250,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan Najeriya.
Asali: Legit.ng