Gwamnatin Tinubu da Ƴan Kwadago Sun Gama Taron Gaggawa Kan Mafi Ƙarancin Albashi
FCT Abuja - Rahotanni sun bayyana cewa an ƙarkare taron gaggawa da gwamnatin tarayya ta kira ƴan kwadago kan yajin aikin da aka fara yau.
Idan baku manta ba muna kawo rahoton cewa shugabannin ƴan kwadago sun isa ofishin sakataren gwamnatin tarayya domin shiga taron gaggawa da aka gayyace su.
TVC News ta kawo cewa a halin yanzun gwamnati da ƴan kwadago sun ƙarkare taron na yau Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.
Sai dai har kawo yanzu ƴan jarida na jiran bayanai daga ɓangarorin da suka halarci zaman, wanda aka shirya da nufin kawo ƙarshen yajin aikin ma'aikata.
Ku saurari ƙarin bayani...
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng