Gwamna Uba Sani Ya Ba da Umurni da Aka Kammala Daukar Mahajjata 4000 a Kaduna
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Jihar Kaduna - Gwamantin jihar Kaduna ta sanar da kammala jigilar mahajjatan jihar zuwa kasa mai tsarki.
A jiya Litinin, 3 ga watan Yuni ne aka ɗauki rukunin karshe na mahajjatan su 300 zuwa kasar Saudiyya.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Amirul Hajji na jihar kuma Sarkin Lere, Mai martaba Sulaiman Umar ne ya jagoranci tawagar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
A lokacin da ake bankwana da alhazan, gwamnan jihar wanda Amirul Hajji ya wakilta, ya ce ya kamata jami'an hukumar alhazai su tabbatar da mutanen Kaduna sun samu kulawa.
Ya ce kamar yadda aka tanadar musu da wuraren zama masu kyau, ya kamata sauran abubuwa ma su tafi lafiya ta inda ba za su ji kamar sun kashe kudinsu a banza ba.
Amirul Hajji na jihar, mai martaba Sulaiman Umar ya ce ya kamata mahajjatan su san cewa za su tafi ibada ne.
Saboda haka su tabbatar sun yi komai cikin koyarwar addini kuma su yi biyayya ga malamai masu wa'azi da sauran jami'an gwamnati.
Shugaban hukumar alhazai ta jihar, Malam Salisu S. Abubakar ya yi godiya ga daukacin wadanda suka taimaka wajen ganin jigilar mahajjatan ta tafi cikin nasara.
Ya kara da godiya ga mahajjatan kan hadin kai da suka ba gwamnatin da ma'aikatan jirgin sama wajen bin ka'idodi da aka gindaya musu.
A wani rahoton, kun ji cewa gwamna Inuwa Yahaya ya amince da bai wa kowane mahajjaci tallafin N500,000 sakamakon ƙarin kuɗin hajjin 2024.
Mai magana da yawun gwamnan, Ismaila Uba Misilli, ya ce wannan matakin zai taimaka wajen ragewa alhazan raɗaɗin matsin tattalin arziki.
Asali: Legit.ng