Home Back

Sarkin Ningi Ya Koka Kan Matsalar Wutar Lantarki A Ƙaramar Hukumar Ningi

leadership.ng 2 days ago
Sarkin Ningi Ya Koka Kan Matsalar Wutar Lantarki A Ƙaramar Hukumar Ningi

Mai Martaba Sarkin Ningi, Alhaji Yunusa Muhammadu Danyaya, ya bayyana takaicinsa kan matsalar wutar lantarki da ake yawan samu ta hanyar sakaci ma’aikatan JEDC.

Sarkin ya nuna damuwarsa ne a lokacin da ya gayyaci jami’an hukumar ta JED zuwa fadarsa, kan rashin wutar lantarki a garin Ningi, inda ya bayyana cewa Ningi ta cancanci samun wutar lantarki mai inganci saboda yawanta mutane da ayyukan kasuwanci a yankin da ma tarihin da take da shi.

A nasa martanin, Manajan tashar JED na Ningi, Sani Ya’u Sallau, ya bayyana cewa sun damu da yadda ake satar wayoyi da sauran na’urorin lantarki a garin na Ningi.

Sallau ya tabbatar wa sarkin cewa su na iya bakin ƙoƙarin ganin sun shawo kan wanna matsalar.

People are also reading