Home Back

An saki sarkin da ya mika kansa kan zargin kisan sojoji 17 a Delta

dailynews24.ng 2024/5/13

Hukumomin sojin Najeriya sun saki Sarkin da aka ayyana nemansa ruwa a jallo bisa zargin hannu kisan dakarun soji 17 a Okuama da ke Ƙaramar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta.

Aminiya ta ruwaito yadda rundunar soji ta ƙaddamar da farautar waɗanda ake zargi da aikata munanan aika-aikar da ta sa mazauna garin Okuama suka fice daga cikin unguwannin garin.

Jim kaɗan bayan samamen da jami’an suka kai, sojoji sun bayyana sunayen: Arthur Ekpekpo, farfesa; Andaowei Dennis Bakriri, Akevwru Daniel Omotegbono (wanda aka fi sani da Amagbem); da Akata Malawa David, waɗanda ake nema ruwa a jallo.

Sauran mutanen da aka bayyana sunayensu sun haɗa da: Sinclear Oliki, da Clement Ikolo Ogenerukevwe da Reuben Baru, da Igoli Ebi, mace ɗaya tilo a cikin waɗanda ake nema ruwa a jallo.

Bayan sanarwar sojojin, Sarkin wanda lamarin ya faru a yankinsa mai suna Clement Ikolo Ogenerukevw ya miƙa kansa ga ‘yan sanda, inda su kuma suka miƙa shi ga sojoji.

Yayin da yake miƙa shi ga Sanata mai wakiltar Delta ta tsakiya a hedikwatar rundunar a ranar Juma’a, Nwachukwu ya ce Sanatan ya shaida halin kirki na sarkin.

People are also reading