Home Back

Narendra Modi ya tsallake rijiya da baya

dw.com 2024/7/3
Firamnistan Indiya Narendra Modi
Firamnistan Indiya Narendra Modi

Sakamakon da aka fitar a yanzu na nuni da cewar jam'iyyar BJP ta firaminista Narendra Modi ta samu gagarumin koma baya, domin kuwa ba za ta samu gagarumin rinjayen da take bukata ba a majalisar dokoki wanda masana ke cewa da alama hakan ka iya kawo mata tangarda wajen tabbatar da manufofinta na kafa cikakkiyar gwamnati.

Karin bayani :  Manoma a Indiya sun bukaci karin farashi

Sakamakon na nuni da cewa jam'iyyar 'yan hamayyar Indiya ta kara ninka kujerunta a zaben inda ake hasashen adadinsu na ninka har sau biyu bayan da ta samu ruwan kuri'u a sassa da dama na kasar Indiya.

Firaminista Modi mai shekaru 73 da aka sake zaba a mazabar sa ta Varanasi, ya bayyana cewa al'ummar Indiya sun kada wa jam'iyyarsa kuri'a da gagarumin rinjaye, sun kuma nuna na'am da sauye-sauyen da ya aiwatar.

People are also reading