Kotu ta Daure Matashin da Ya Sace Dabbobi, ya Kalmashe Kudin Mutane a Aljihu
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Ogun - Wata kotu da ke zamanta a Abeokuta ta kama wani matashi mai shekaru 35, Kabiru Lawal da laifin zambar rago da tumaki sannan ya cefanar da su ya kalmashe kudin.
Matashin mazaunin Olomore a garin Abeokuta ya shaidawa kotu cewa da gaske shi ne ya yi dan hali, bayan ya ci amanar mai dabbobin sannan ya kai su kasuwa ya sayar.
Vanguard News ta wallafa cewa mai shari’a Mrs V.B. William ta yi masa daurin watanni uku-uku na dukkanin laifukan biyu, watau samun dabbobin ba bisa ka’ida ba da sayar da su.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mai shari’a V.B. William a yau ta bawa matashin nan da aka tabbata ya sace rago da tumaki ta hanyar zamba zabin ya biya kudinsu ko ya yi zaman gidan yari da dukkanin laifuka biyu da aka kama shi da su.
A zaman kotun na yau Juma’a, mai shari’ar ta ce zai iya lissafa kudin dabbobin sannan ya biya mai dukiyar, ya kuma yi tafiyarsa.
Pulse.ng ta wallafa cewa tun a shekarar 2023 ake zargin Lawal da lallaba mai dabbobin inda ya kwashe tumaki takwas da rago guda da kudinsu ya kai N300,000 bayan ya ce zai sayar masa da su.
Bayan ya karbi dabbobin tare da sayar da su ne sai ya gudu ya bar jihar Ogun baki daya kafin daga bisani a samu nasarar kama shi.
A baya kun ji cewa wasu barayin raguna sun shiga hannun hukuma su na tsaka da kokarin cefanar da ragunan da su ka sato a gida wani Alhaji a babban birnin tarayya Abuja.
Asali: Legit.ng