Home Back

Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano

leadership.ng 2024/5/17
Kwale-kwale Ya Yi Ajalin Dalibai 2 A Kano

Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, ta tabbatar da nutsewar dalibai biyu na Kwalejin Aikin Gona ta Audu Bako da ke karamar hukumar Makoda a wani Dam.

Kakakin hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, Saminu Abdullahi, wanda ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, ya ce lamarin ya shafi dalibai uku, amma ya ce an ceto wani mai suna Ibrahim.

A cewar sanarwar, “A ranar Talata 30 ga watan Afrilu, 2024, hukumar kashe gobara ta jihar da ke karamar hukumar Danbatta ta samu kiran agaji da misalin karfe 3:06 daga Kwamared Ibrahim Muhammad wanda ya sanar da faruwar lamarin.

“Bayan isa wajen, sun tarar da dalibai uku da ke karatu a Kwalejin Aikin Gona ta Audu Bako da ke karamar hukumar Makoda wadanda suka shiga kwale-kwale da niyyar tsallakawa, amma suka nutse.

“Cikin ikon Allah matukin kwale-kwalen ya yi nasarar ceto daya daga cikin daliban mai suna Ibrahim mai shekaru 21.”

Abdullahi ya kara da cewa jami’an hukumar da masunta a yankin sun yi nasarar ceto dalibai biyu; Abubakar Sanusi mai shekaru 22 sa Salisu Ado mai shekaru 21.

Ya bayyana cewa da fari an ceto daliban a sume, amma daga baya likitoci suka tabbatar da rasuwarsu.

Abdullahi ya ce an kwantar da wanda ya kubuta a babban asibitin garin Danbatta, inda yake ci gaba da murmurewa.

People are also reading