Home Back

Takarar Biden na kara fuskantar barazana

dw.com 2024/8/21
Takarar Biden na kara fuskantar barazana
Takarar Biden na kara fuskantar barazana

Tsaffin 'yan majalisar wakilan Amurka na jam'iyyar Democrat sama da 20 sun wallafa wata wasika a ranar Juma'a suna masu neman Shugaba Joe Biden da ya kira babban taron tattaunawa da 'ya'yan jam'iyyar domin bai wa sauran masu sha'awar tsayawa takara a zaben kasar na watan Nowamba damar gabatar da kansu.

A  cikin budadiyar wasikar, staffin jiga-jigan jam'iyyar ta Democrat sun ce idan har mista Biden na son hidimtawa Amurka ya zama wajibi ya dakatar da yunkurin yin gaban kansa domin barin wakilan jam'iyyar sun ayyana shi a matsayin wanda zai tsaya takara a karo na biyu.

Wasikar ta kuma ce mutumcin shugaban da hangensa na nesa na jagoranci bai disashe ba, amma kuzari da karfin da yake bukata domin gudanar da yakin neman zabe har ma da jan ragamar Amurka a wa'adin mulki na biyu sun ragu.

Tun bayan mahawarar da ya yi da abokin hamayarsa Donald Trump, Shugaba Joe Biden mai shekari 81 a duniya ke fuskantar zazzafar suka daga makusantansa tare da kiransa da ya janye daga tsayawa takara, yayin da shi kuma ke cewa babu gudu babu ja baya.

People are also reading