Sallah: Matawalle Ya Gwangwaje Zamfarawa da Raguna, Ya Raba 390m
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Zamfara - Gabanin bikin Eid-el-Kabir na 2024, tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma ƙaramin ministan tsaro, Bello Mohammed Matawalle ya raba raguna 4,860 ga al'ummar jihar.
Ƙaramin ministan ya kuma ware Naira miliyan 390 domin rabawa magoya bayan jam’iyyar APC da masu ƙaramin ƙarfi wanda hakan na daga cikin al’adarsa a lokacin irin waɗannan bukukuwa a jihar.
Jaridar Tribune ta ce waɗanda suka ci gajiyar tallafin sun haɗa da mambobin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC na jihar da kuma shugabannin jam’iyyar a matakin ƙananan hukumomi da mazaɓu a ɗaukacin ƙananan hukumomin jihar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sauran waɗanda suka ci gajiyar tallafin sun haɗa da dattawan jam’iyyar, matasa, ƙungiyoyin mata, malamai, marasa galihu, marayu da gajiyayyu da kuma ƴan jam’iyyar APC a faɗin jihar.
Sauran sun kasance tsofaffin masu muƙami a gwamnatin Matawalle da suka haɗa da kwamishinoni, masu ba da shawara na musamman, da manyan daraktoci.
Sauran sune manyan mataimaka na musamman, mataimaka na musamman, mambobin hukumomi da sauransu.
Hakazalika, an zaɓo mutane 140 daga ƙananan hukumomi 14 na jihar tare da ba su Naira 100,000 kowannensu domin tallafa musu a yayin bikin Sallah.
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na Tinubu/Shettima 2023 a jihar Zamfara, Sanata Kabiru Marafa ya caccaki ƙaramin ministan tsaro, Bello Matawalle.
Kabiru Marafa ya caccaki tsohon gwamnan na jihar Zamfara ne kan kiran Dattawan Arewa a matsayin wani nauyi da ya damu ƴan Arewa.
Asali: Legit.ng