Sojoji Sun Ceto Wadanda Aka Yi Garkuwa da Su a Arewacin Najeriya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Sojojin Najeriya sun yi nasarar wargaza sansanin 'yan ta'adda a jihar Taraba tare da kubutar da wadanda aka yi garkuwa da su.
Hukumar sojin ta bayyana haka ne ta bakin jami'in ta na hulda da jama'a, Laftanal Oni Olubodunde, ranar Talata.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa sojojin sun kai hari wa ƴan ta'addan ne bayan wasu bayanan sirri da suka samu.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Sun samu bayanan ne kan wata maboyar ƴan ta'addan da ke garkuwa da mutane a Punkun cikin karamar hukumar Ussa.
Rundunar sojan ta ce sun yi nasarar wargaza maboyar ta su tare da kwato bindigogi da sauran makamai.
Dadin dadawa rundunar ta yi nasarar cafke wani mai suna Dogo Manu da ake zargin mai garkuwa da mutane ne a yankin, cewar jaridar Tribune
A jihar Filato ma rundunar sojin ta yi nasar ceto mutane biyu da aka yi garkuwa da su a yankin Maraban Jama'a.
Majo Nantip Kakhom ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a jiya Talata, 30 ga watan Afrilu.
Ya ce sojojin an kira su ne ta waya a kan cewa an yi garkuwa da mutane kuma suka amsa kiran cikin gaggawa.
A lokacin da suka amsa kiran sun yi nasarar ceto Abdul Bello da Keyen Melody Yapshak daga hannun masu garkuwa da mutanen.
A wani rahoton, kun ji cewa dakarun Operation Forest Sanity dake jihar Zamfara sun samu nasarar ceto wasu mutum uku daga masu garkuwa da mutane bayan sun je sintiri maboyarsu
Sojojin sun garzaya har kauyen Danmarke dake karamar hukumar Gummi inda suka sakarwa 'yan bindigar wuta wanda hakan yasa suka arce da raunikan bindiga
Asali: Legit.ng