Home Back

Kwale Kwale Ya Kife da Masu Tserewa Harin 'Yan Bindiga a Neja, Mutum 4 Sun Rasu

legit.ng 2024/7/1

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Neja - Wani kwale-kwale da ke ɗauke da wasu mazauna ƙauyukan da ke tserewa hare-haren ƴan bindiga a jihar Neja ya kife.

Mutanen dai sun fito ne daga ƙauyen Gurmana da ke ƙaramar hukumar Shiroro a jihar Neja.

Mutum hudu sun rasu a Neja
Kwale Kwale da masu tserewa 'yan bindiga a Neja Asali: Original

Jaridar Leadership ta kawo rahoto cewa bayan kifewar kwale-kwalen, mutum huɗu sun rasa rayukansu.

Mutanen ƙauyen sun gudu zuwa wani tsibiri ne domin buya daga ƴan bindiga a daren ranar Laraba bayan ƴan bindigan sun kawo hari.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kifewar kwale-kwalen ta auku ne a ranar Alhamis lokacin da suke dawowa bayan da ƴan bindigan suka gama kai farmaki a ƙauyukan.

An tattaro cewa mutanen ƙauyen suna zuwa tsibirin ne da ke tsakiyar kogin Kaduna domin ɓuya daga ƴan bindigan waɗanda suke jin tsoron kogin.

Ƴan bindigan sun kashe mutum uku a hare-haren na daren jiya, sannan sun sace shanu masu yawa tare da yin awon gaba da mutane da dama a Bassa kusa da Gurmana.

Asali: Legit.ng

People are also reading