Home Back

Ana Tsaka da Rigimar Kano, Rikici Ya Kaure Tsakanin Masu Nadin Sarki a Wata Jiha

legit.ng 5 days ago
  • Masu nadin sarki a yankin Ifon da ke karamar hukumar Ose a Ondo sun koka kan yadda ake kokarin ƙaƙaba musu wani a matsayin sarki
  • Sakatarensu, Kehinde Falowo shi ya tabbatar da haka a yau Alhamis 27 ga watan Yunin 2024 inda ya zargi wasu ƴan siyasa
  • Wannan na zuwa ne yayin da rikici ya barke a tsakaninsu da rarrabuwar kawuna kan wanda zai kasance sarkin yankin

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ondo - Rikici ya barke tsakanin masu nadin sarki a kauyen Ifon da ke karamar hukumar Ose a jihar Ondo.

Hakan ya biyo bayan rarrabuwar kawuna tsakanin masu nadin sauratar kan wanda ya kamata a nada sarki a yankin.

An kaure tsakanin masu nadin sarki bayan ƴan siyasa sun tsoma baki
Rikici ya barke tsakanin masu nadin sarki a jihar Ondo Asali: Original

Ondo: An zargi ƴan siyasa da hannu

Wani tsagi na masu nadin sarki sun zargi kokarin tilasta musu Prince Adelanke Odogiyon a matsayin Sarki, cewar Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sun zargi wasu daga mukarraban gwamnati da neman kakaba musu Odogiyon domin biyan buƙatar kansu.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren masu nadin Sarkin, Kehinde Falowo ya fitar a ya Alhamis 27 ga watan Yunin 2024.

Ondo: Kotu ta rusa sabbin ƙananan hukumomi

A wani labarin, kun ji cewa wata Babbar Kotun jihar Ondo da ke zama a Akure ta rusa dokar da marigayi Oluwarotimi Akeredolu ya zartar na kirkirar karin kananan hukumomi 33.

Alkalin kotun Mai Shari'a, Adegboyega Adebusoye ya yanke wannan hukuncin a ranar Alhamis 20 ga watan Yunin 2024 da muke ciki.

Adegboyega Adebusoye ya ayyana kirkirar kananan hukumomin a matsayin abin da ya sabawa kundin tsarin mulki kuma ya sabawa ka’ida.

Asali: Legit.ng

People are also reading