DMO: Jihohi Sun Rage Karbo Rancen Cikin Gida Yayin da Kudin da Ake Bin Najeriya ya Karu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Abuja- Ofishin kula da basussuka (DMO) ya bayyana cewa an samu raguwar basussukan cikin gida da jihohin kasar nan 35 suka karba a watanni ukun farko na 2024.
Alkaluman da DMO ya fitar sun bayyana cewa kudin ya ragu da N1.79trn idan aka kwatanta da watannin baya da basussukan cikin gida suka kai N5.86trn a watan Disamba, 2023.
The Cable ta wallafa cewa a bayanan da aka tattaro a watan Maris 2024, basussukan da aka karbo daga cikin gida ya kai N4.07trn wanda ke nuna samun ragin N1.79trn.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Binciken da aka gudanar ya tabbatar da jihar Jigawa ce kan gaba a jihohin kasar nan da suka rage karbo basussuka a cikin gida a farkon shekarar nan.
Jihohin Arewa maso Yamma sun rage basussukan cikin gida da suka karbo da 95%, wanda ya kai N40.69bn, yayin da jihohin Onda da Kebbi suka rage na su da 77%, wanda ya kai N55.11bn da kuma 72% da ya kai 61.25bn.
Jihohin kasar nan 35 ne suka yi kokari wajen rage karbo basussukan cikin gida a farko-farkon shekarar 2024; ga jerin jihohin da kason da suka rage na karbo basussuka;
1.Jigawa: -95%
2. Ondo: -77%
3. Kebbi: -72%
4. Ebonyi: -68%
4. Kogi: -68%
6. Nassarawa: -67%
7. Kaduna: -66%
8. Borno: -63%
9. Katsina: -62%
10. Taraba: -60%
11. Anambra: -54%
12. Ekiti: -48%
13. Kano: -47%
14. Kwara: -46%
14. Yobe: -46%
16. Edo: -42%
17. Zamfara: -41%
18. Osun: -40%
19. Benue: -38%
19. Niger: -38%
19. Oyo: -38%
19. Plateau: -38%
19. Sokoto: -38%
24. Bauchi: -33%
25. Bayelsa: -32%
26. Cross River: -29%
27. Adamawa: -25%
27. Akwa Ibom: -25%
27. Imo: -25%
30. Ogun: -21%
31. Gombe: -20%
32. Abia: -18%
33. Enugu: -11%
33. Lagos: -11%
35. Delta: -10%
A wani labarin kun ji cewa basussukan da ake bin Najeriya ya karu bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya karbo rancen N6.35tn tsakanin Disambar 2023 zuwa Maris 2024.
Basussukan sun karu saboda rancen da gwamnatocin jihohin kasar nan, gwamnatin tarayya da Abuja suka karbo a cikin watannin uku na shekarar 2024.
Asali: Legit.ng