Home Back

Kasashen Turai na shirin zaben shugaban EU

dw.com 2024/6/30
Shugabar hugabar EU, Ursula von der Leyen
Shugabar hugabar EU, Ursula von der Leyen

Shugabar hukumar Turan ta yanzu Ursula von der Leyen, 'yar siyasar Jamus na neman goyon baya a wa'adi na biyu da take nema.

Jam'iyyarta ta European Peoples Party EPP a majalisar ta samu nasara a zaben Turai da aka kammala a baya-bayan nan.

Hakan dai na nuna alamun Ursula von der Leyen na iya kai labari a wa'adi na biyu na shekaru biyar da take son tsayawa takara.

Sai dai a bayyane take tana bukatar samun goyon baya daga wasu kungiyoyi na siyasa a majalisar.

A ranakun 27 da 28 ne dai za a gudanar da zaben na kungiyar EU duk da cewa akwai alamun samun dan takara babu hamayya.

People are also reading