Home Back

Kwana 1 da Lashe Gasar Champions League, Madrid Ta Sayi Mbappe Daga PSG

legit.ng 2024/9/29

Shahararren dan wasan Faransa, Kylian Mbappe ya koma kungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid bayan sanya hannu a kwantiragi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Paris - Dan wasan gaban Faransa, Kylian Mbappe ya sanya hannu a kwantiragi da kungiyar ƙwallon ƙafa ta Real Madrid.

Dan wasan mai shekaru 25 ya jona Madrid ne kwana ɗaya bayan sun lashe gasar zakarun Turai ta Champions League.

Dan jarida daga kasar Italiya, Fabrizio Romano shi ya tabbatar da haka a shafinsa na X a yau Lahadi 2 ga watan Mayu.

Romano ya ce an kammala dukkan wasu ka'idoji kan kwantiragin inda Mbappe ya sanya hannu.

"Kylian Mbappe zuwa Real Madrid ta tabbata, duk wata takarda ta kwantiragi an tabbatar da ita kuma an sanya hannu."

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Real Madrid za ta sanar da siyan Mbappe a matsayin sabon ɗan wasanta a makon gobe bayan lashe gasar Champions League."
"Mbappe ya yanke shawarar barin PSG a watan Faburairu, yanzu za a iya cewa ya dawo sabon ɗan wasan Real Madrid."

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

People are also reading