Home Back

Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

leadership.ng 2024/5/18
Haaland Ba Zai Samu Buga Wasan Man City Da Brighton Ba A Yau Alhamis

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Erling Braudt Haaland ba zai sami damar buga wasan da Manchester City zata ziyarci Brighton a wasan mako na 29 da ya zama kwantai a watan jiya.

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Manchester City, Pep Joseph Guardiola ne ya bayyana haka ga manema labarai yayin daukar atisayen kungiyar gabanin wasan da zasu fafata a yau Alhamis a filin wasa na American Express Stadium da ke Brighton.

Haaland ya zama zakaran gwajin dafi a wasannin gasar Firimiya inda yanzu haka ya jefa kwallaye 20 a gasar, shine ya lashe kyautar takalmin zinare a kakar wasan da ta gabata da kwallaye 36.

City na fatan ganin ta doke Brighton a wasan yau domin matsowa kusa da masu jan ragamar gasar Firimiya Arsenal wadda ta yi wa Chelsea kaca kaca a makon jiya.

People are also reading