Home Back

Kotu Ta Kora Babban Jami'in Kamfanin Binance Zuwa Gidan Gyaran Hali

legit.ng 2024/5/12
  • Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bada umurnin a tsare babban jami'in kamfanin Binance, Tigran Gambaryan, a gidan gyaran hali na Kuje
  • Alƙalin kotun mai shari'a Emeka Nwite ne ya bada wannan umurnin har zuwa lokacin da za a yi hukunci kan belin da Gambaryan ya nema
  • Za a dawo da Gambaryan gaban kotun a ranar, 18 ga watan Afirilu domin zartar da hukunci kan buƙatarsa ta neman beli

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin tsare babban jami’in Binance, Tigran Gambaryan, a gidan gyaran hali na Kuje.

Kotun ta umurci a tsare Gambaryan ne har zuwa lokacin da za ta yi hukunci kan belin da ya nema, cewar rahoton jaridar The Punch.

Kotu ta tsare jami'in Binance
Kotu ta umurci a tsare jami'in Binance a gidan gyaran hali Hoto: Economic and Financial Crimes Commission Asali: Facebook

Alƙalin kotun, mai shari’a Emeka Nwite, ya bayar da umarnin ne bayan Gambaryan ya ƙi amsa laifin safarar kuɗaɗe da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa da ya yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) ke yi masa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wace tuhuma ake yi wa Gambaryan?

EFCC na zargin kamfanin Binance, Gambaryan, da Nadeem Anjarwalla wanda ya arce kan ɓoye hanyar da suka samu $35,400, 000 a matsayin kuɗin shiga a Najeriya.

Lauyan masu shigar da ƙara ya buƙaci a sanya ranar da za a fara shari'ar. Sai dai lauyan Gambaryan ya roƙi kotun da ta bayar da belin wanda yake karewa.

Daga bisani alƙalin kotun ya ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 18 ga watan Afrilu domin yanke hukunci kan belin da ya nema da kuma ranar 2 ga watan Mayun 2024, rahoton jaridar Vanguard ya tabbatar.

Jami'in Binance ya shigar da ƙara

A wani labarin kuma, kun ji cewa jami'in kamfanin Binance da ke tsare a Najeriya ya maka mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu da hukumar EFCC a gaban kotu.

Tigran Gambaryan ya shigar da ƙarar ne bisa abin da ya kira tauye masa haƙƙinsa da aka yi kan ci gaba da tsare shi da ake yi.

Asali: Legit.ng

People are also reading