Sallah: Kwankwaso Ya Faɗawa Gwamna Abba Muhimmin Abu 1 da Ya Kamata Ya Yi a Kano
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kano - Jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Kwankwaso ya shawarci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya mayar da hankali wajen gina al'umma.
Kwankwaso ya ba shi wannan shawara ne yayin da Gwamna Abba da wasu muƙarrabansa suka kaiwa jagoran NNPP ziyarar Barka da Sallah.
Ya yabawa gwamnan bisa ƙwazon da ya yi a shekararsa ta farko a kan kujerar mulkin Kano, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawun gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Litinin.
An tattaro cewa Kwankwaso ya yaba da kokarin gwamna Yusuf wajen bunƙasa ilimi da karfafa mata gwiwa da nufin inganta rayuwar mazauna jihar Kano.
Kwankwaso ya nuna jin dadinsa kan yadda Gwamna Abba ke tallafawa mata da goyon bayansu, wanda ya yi daidai da aƙidar Kwankwasiyya.
Ya buƙaci gwamnatin Abba ta kara zage dantse wajen tabbatar da tsaro, taimakawa masu ƙarafin ƙarfi da kuma gina ayyukan raya ƙasa.
Tsohon gwamnan ya ce ƙofarsa a buɗe take wajen bayar da shawarwari da kuma goyon bayan gwamnati idan hakan ta taso.
A nasa jawabin, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya godewa Kwankwaso bisa shawarwari da nasihar da yake masa.
Gwamnan ya kuma jaddada kudirin gwamnatin san bin ƙa'idoji da aƙidar ɗarikar Kwankwasiyya domin ɗaga martabar jihar Kano da kawo ci gaba mai ɗorewa.
A wani rahoton kuma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya fara samun goyon baya daga shugabannin siyasa gabanin babban zaɓen 2027.
Jagororin jam'iyyar APC a shiyyar Kudu maso Kudu sun bukaci Tinubu ya sake neman takara karo na biyu a zaɓe mai zuwa.
Asali: Legit.ng