Gwamnatin Tinubu Ta Tsoma Baki Kan Rikicin Iran da Isra'ila
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - A yayin da ci gaba da rikici tsakanin Iran da Isra’ila, ƙasashe musamman na yammacin duniya sun yi kira da a tsagaita buɗe wuta.
Ƙasashen sun kuma yi kira da a hau teburin sulhu domin kawo ƙarshen rikicin da ke neman ƙara yaɗuwa.
A nata ɓangaren, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bakin ma'aikatar harkokin wajen ƙasar nan ta buƙaci ƙasashen Iran da Isra'ila da su yi haƙuri da juna.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Gwamnatin ta buƙaci hakan ne domin gujewa ɓarkewar rikici a yankin Gabas ta Tsakiya.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata ƴar gajeruwar sanarwa da ma'aikatar ta fitar a ranar Lahadi,14 ga watan Afrilu mai ɗauke da sa hannun kakakinta, Fransisca Omaluyi.
Ma’aikatar ta bayyana cewa, a cikin wannan lokaci, ya zama wajibi ƙasashen biyu su yi tunani a kan ƙudurin da ƙasashen duniya suka ɗauka na warware rikice-rikice cikin lumana domin ci gaban zaman lafiya da tsaro a duniya.
Wani ɓangare na sanarwar na cewa:
"Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bi sahun sauran ƙasashen duniya wajen yin kira ga Iran da Isra’ila da su yi taka-tsantsan, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya na kwantar da hankula da kaucewa ɓarkewar rikici a Gabas ta Tsakiya."
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban ƙasar Amurka ya nesanta kansa kan shiga cikin Iran da Isra'ila.
Joe Biden ya bayyana cewa Amurka ba za ta taimakawa Isra'ila ba ta kai hari kan ƙasar Iran a rikicin da ƙasashen biyu ke yi.
Asali: Legit.ng