Home Back

Ondo: Jam'iyyar APC Ta Ayyana Zaben Fidda Gwanin Jihar 'Inconclusive', Ta Fadi Dalilai

legit.ng 2024/5/18

Yayin da ake gudanar da zaben fidda gwani a jihar Ondo, jam'iyyar APC ta ayyana zaben wanda bai kammala ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Ondo - Jam'iyyar APC ta ayyana zaben fidda gwanin jihar Ondo wanda bai kammala ba.

Jam'iyyar ta dauki matakin ne bayan samun rahotanni daga unguwanni 203 da kuma kananan hukumomi 18.

Shugaban kwamitin zaben fidda gwanin, Gwamna Usman Ododo na jihar Kogi shi ya tabbatar da haka, cewar rahoton AIT.

Ododo ya ce zaben bai gudana ba a wasu ƙananan hukumomi saboda rashin kawo kayan zaben da kuma masu gudanarwa saboda wasu matsaloli.

Ya ce za a gudanar da zaben fidda gwanin a unguwannni 13 da ke karamar hukumar Okitipupa da misalin karfe 12:00 na a yau Lahadi 21 ga watan Afrilu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Yankin na dauke da mambobin da suka yi rijista da suka kai akalla 9,515 wadanda za su gudanar da zaben a karamar hukumar.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

People are also reading