Sanata Barau Ya Yi Magana Kan Mutuwar Mutum 14 a Masallacin Jumu'a a Kano
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Jihar Kano - Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I Jibrin, ya yi ta'aziyyar rasuwar masallata 14 da motar tirela ta bi ta kansu ranar Jumu'a a Kano.
Lagit Hausa ta kawo muku rahoton yadda babbar motar ta bai ta kan masallatan jim kaɗan bayan sallame Sallar Jumu'a a garin Imawa da ke ƙaramar hukumar Kura.
Hukumar kiyaye haɗurra ta kasa (FRSC) ta tabbatar da mutuwar Musulman sakamakon haɗarin wanda direban tirelar ya gaza shawo kan motar da misalin ƙarfe 13.50 na rana.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kamar yadda Daily Trust ta ruwatu, Sanata Barau ya nuna damuwa bisa faruwar ibtila'in, inda ya aike da saƙon ta'aziyya ga iyalaan mamatan.
Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ismail Mudashir ya fitar ranar Asabar.
Sanata Barau ya kuma yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya tashi kafaɗun wadanda suka jikkata cikin kankanin lokaci.
"Cikin yanayin jimami muna alhinin rasuwar masallata 14 waɗanda wata tirela ta murkushe bayan sallar Juma’a a Kano. Muna mika sakon ta'aziyya ga iyalai da abokan arziki.
"Muna addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu ya sa sun huta kuma muna rokon Allah ya sa su a gidan Aljanatul Firdausi."
"Muna rokon Allah maɗaukakin sarki ya bai wa iyalansu haƙuri da juriyar wannan babban rashi."
- Barau Jibrin.
A wani labarin kuma Wani gini da ake kan aiki a Kuntau da ke cikin kwaryar birnin Kano ya rufta kan ma'aikata da wasu mutane ranar Jumu'a.
Rahotanni sun bayyana cewa ginin ya danne mutane 5 ciki hada mai gidan kuma ana fargabar takwas daga ciki sun rasu.
Asali: Legit.ng