Home Back

Ministar harkokin wajen Jamus za ta kai ziyara Afirka

dw.com 2024/8/23
Annalena Baerbock

Ministar harkokin wajen Jamus za ta gana da sabon shugaban kasar Senegal Bassirou Jiomay Fay ne a ranar Litinin a Dakar fadar gwamnatin kasar.

A ranar Talata ne kuwa babbar jami'ar diflomasiyyar Jamus din za ta isa Abidjan na Ivory Coast, inda za ta gana da Shugaba Alassane Ouattara. Daga cikin batutuwan da ziyarar Baerbock za ta maida hankali a kai, har da abin da ya shafi makamashi da ake sabuntawa da kuma shige-da-fice.

Yayin dai da wasu kasashen yammacin Afirka suka raba gari da ECOWAS da kasashen yamma, kasashen Senegal da Ivory Coast na ci gaba da yaukaka dangantakarsu da kasashen yammacin na duniya.

People are also reading