Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Fiye Da Naira Biliyan 2 Domin Ciyarwa A Watan Ramadan
Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da kashe Naira biliyan 2.8 domin ciyar da mabukata da marasa karfi a jihar a watan Ramadan.
Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis a Dutse.
Musa ya ce, an dauki matakin ne a taron majalisar zartarwa na jihar da ya gudana a ranar Laraba, 13 ga watan Maris.
Ya ce, an amince da shirin ne domin tallafawa al’umma sakamakon hauhawar farashin kayayyakin abinci da ake fuskanta a kasar.
Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da cibiyoyin ciyar da abinci guda 609 a fadin jihar domin ciyar da abincin a watan Ramadan, inda ya ce, akwai a kalla cibiyoyi biyu a kowacce unguwa 287 da ake da su a fadin jihar.