Home Back

Kano: Kwankwaso Ya Fadi Abin da Ya Dauke Hankalin Abba a Shekara 1 Na Mulki

legit.ng 2024/6/30
  • Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya magantu kan irin kokarin 'yan adawa na kawo rudani a jihar a mulkin Abba Kabir
  • Kwankwaso ya zargi jam’iyyun adawa da neman dagula jihar bayan kammala zaben inda suka shiga kotu domin kalubalantar zaben
  • Sanatan ya bayyana haka ne a yau Asabar 8 ga watan Yuni a birnin Kano yayin sanya dokar ta baci a bangaren ilimi

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Jihar Kano – Sanata Rabiu Kwankwaso ya bayyana wadanda suke kawo rudani a jihar Kano musamman a mulkin Abba Kabir Yusuf.

Kwankwaso ya ce makiya jihar Kano ne suke kawo tarnaki domin kauda hankalin gwamnatin jihar cikin shekara daya da ta yi.

Sanatan ya bayyana haka ne a yau Asabar 8 ga watan Yuni yayin taron tabbatar da dokar ta baci a bangaren ilimi a jihar, cewar Daily Trust.

“Zan fara da taya shi murna kan wannan rana mai tarihi, ranar da ake sanya dokar ta baci a bangaren ilimi.”
“Wadanda ba su sani ba, gwamnan yana aiki ba dare ba rana domin inganta jihar kamar yadda kuke gani ya tabo ko ina.”

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

“Duk da yawan dauke hankalinsa da aka yi na shekara daya, bayan kammala zabe, makiya Kano sun maka shi a kotu, mun ga abin da ya faru duk sun sani babu bukatar zuwa kotu saboda kowa ya sani shi ya ci zabe.”

- Rabiu Kwankwaso

Karin bayani na tafe…

Asali: Legit.ng

People are also reading