Home Back

Kotu ta aike da wata mata gidan Yari kan zargin ta da yanke maƙarfafar mijin ta a Kano

dalafmkano.com 2024/7/1

Kotun majistret mai lamba 54 ƙarƙashin jagorancin mai Shari’a Ibrahim Mansur Yola a jihar Kano, ta fara sauraron wata ƙara wadda ƴan sanda suka gurfanar da wata mata mai suna Maryam Imam mazauniyar garin Tofa, inda ake zargin ta da laifin yanke makarfafar mijinta Abubakar Imam.

Yayin da aka karanta wa matar ƙunshin tuhumar da ake mata ta amsa nan take, ta kuma shaidawa Alkalin kotun cewar tun farko auren dole akayi mata, kuma shi mai gidan nata duk da yasan cewar bata kaunarsa amma kullum sai ya ɓata mata rai.

Mai Shari’a Mansur Yola ya ayyana cewar za a yi hukunci ranar 11/6/2024 dan gudun nama ya dawo romo ɗanye, tunda dai ance Abubakar din yana kwance a asibiti yana ci gaba da samun kulawar likitoci.

Kotun ta kuma umarci a ajiye matar a gidan gyaran hali zuwa waccan ranar da aka sanye domin yanke hukuncin.

Wakilunmu Yusuf Nadabo Ismail ya so zantawa da matar da ake zargi da yankewa mijin nata maƙarfafa, sai dai dogarawan gidan gyaran hali sun shiga tsakani, hakan ya sa lamarin ya gagara.

People are also reading