Home Back

Venezuela janye gayyatar jami'an EU a zabenta

dw.com 2024/7/2
Shugaba Nicolas Maduro na Venezuela
Shugaba Nicolas Maduro na Venezuela

Gwamnatin ta Venezuela ta kafa hujja da abin da ta kira takunkuman mulkin mallaka da Tarayyar ta kakaba wa kasar a matsayin hujjar janye gayyatar da ta yi wa jami'an.

Tarayyar Turan daga nata bangaren, wacce ta kakaba wa Venezuela takunkumai a shekarar 2017, ta yi kira ga kasar da ta sake nazarin wannan mataki da ta dauka.

Shugaba Nicolas Maduro na Venezuela dai na neman zabe karo na uku, ya yin da tsohon jami'in diflomasiyya Edmundo Gonzalez ke wakiltar gamayyar jam'iyyun hamayya.

Shugaba Maduro tun da fari, ya amince da karbar baki masu sa ido daga ketare, yayin kuma da a gefe guda yake tsananta wa 'yan hamayya a kasar.

People are also reading