Home Back

Gina gadar naira biliyan 27 a Kano, tsohon kwamishinan Ganduje ya ragargaji Abba Yusuf

premiumtimesng.com 2024/5/19
Gwamnatin Kano ta hana lika fastoci a ginegine a fadin jihar

Tsohon kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Kano, Muaz Magaji, ya caccaki gwamna Abba Yusuf kan fara aikin gina sabbin gadoji biyu a babban birnin jihar kan kudi naira biliyan 27.

Magaji wanda ya yi aiki a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ya bayyana ayyukan a matsayin abin da ba shi ake buka ta yanzu a Kano ba.

Idan ba a manta ba tun a ranar Lahadin da ta gabata ne Gwamna Yusuf ya aza harsashin ginin daya daga cikin gadar sama a Kofar Dan’agundi da ke cikin birnin Kano, kan kudi Naira biliyan 15. Ya ce ginin zai inganta zirga-zirgar ababen hawa a tsohon birnin, a cewar sanarwar da mai magana da yawunsa, Sanusi Bature ya fitar.

Gwamna Abba ya ce zai mayar da garin kano birni irin na zamani da za a rika alfahari da shi.

Sai dai kuma idan ba a manta ba a ba tsohon gwamnan jihar, Rabiu Kwankwakso, wanda shi ne ubangidan gwamna Yusuf, a watan Maris din shekarar 2021 ya nuna adawa da gina sabbin gadar sama a jihar, yana mai bayyana hakan a matsayin ba abi da Kanawa ke bukata ba ke nan a wannan lokaci.

Sai dai kuma ba kamar tsohon gwamna Ganduje ba da bashi ya rankatako wa jihar kano a lokacin ya gini gadar sama a shataletalen Hotoro, gwamna Abba na yanzu ya ce kudin kananan hukumomi ne zai rika zaftare wa ya narkawa a g

People are also reading