Home Back

Hajjin Bana: Jihar Kebbi Ta Lashe Kambun Gwarzuwar Shekara

leadership.ng 2024/10/5
kebbi

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta ayyana Jihar Kebbi a matsayin jihar da ta fi kowacce jiha aiki cikin tsari da nasara a cikin hukumomkin Alhazai na Nijeriya, Shugaban hukumar, Malam Jalal Ahmed Arabi ne ya bayyana haka a tattaunawsarsa da manema labarai a Jidda ta kasar Saudiya.

Ya ce, Jihar Kebbi ta yi zarra ne a dukkan bangarorin gudanar da aikin Hajji, tun daga jin dadin alhazai daga gida Nijeriya zuwa kasa mai tsarki da samar da ingantaccen masaukai da kuma kula da lafiyar Alhazai.

Sanarwar haka ta fito ne takardar sanarwar da sakataren yada labarai na gwamnan, Alhaji Ahmed Idris ya sanya wa hannu aka kuma raba wa manema labarai a Makkah. “Haka ake fatan ganin dukkan jihohi su kasance, muna fatan sauran jihohi za su yi koyi da Jihar Kebbi don samar wa Alhazai jin dadi a yayin gudanar da aikin Hajji a shekaru mai zuwa. Ina mai amfani da wannan damar don jinjina ga Gwamnan Jihar, Dakta Nasir Idris a kan irin goyon bayan da yake ba Hukumar Alhazai ta jihar a karkashin shugabancin Alhaji Faruku Aliyu-Enabo.

“Ina mai buga kirjin cewa, babu wata jiha da ta kyautata harkokin jin dadin Alhazai kamar Jihar Kebbi,” in ji shi.

People are also reading