Fitaccen Malamin Addini, Alkali Abubakar Zariya Zai Ƙara Aure, Ya Fadi Sunan Amaryarsa
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Jihar Kaduna- Fitaccen malamin addinin Musulunci daga Arewacin Najeriya, Alkali Abubakar Salihu Zariya ya yi magana kan shirin ƙarin auren da ya ke yi.
Alkali Abubakar Zariya ya ce soyayya da yabon da yake yi wa uwar gidansa, Jamila, ba shi zai hana ya auri masoyiyarsa Sumayya ba.
A wata hira da gidan rediyon Freedom da ke Kano, malamin addinin ya ce masu cece-kuce a kan ƙarin auren sun daɗe, domin ba gudu ba ja da baya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce ya na kyautata zaton ƙarin auren zai ragewa Jamila ayyukan cikin gida, haka zalika ba za ta yi zaman mokoki ita kadai idan ya koma ga mahaliccinsa ba.
A bangaren sa shi ma, idan Allah ya fara karbar rayuwar Jamila, zai samu saukin raɗaɗin mutuwar saboda yana da Sumayya.
A cewar Alkali Abubakar Zariya:
"Yabon da nake yi wa Hajiya Jamila ba zan daina ba, haka kuma ƙarin auren ba zan fasa ba sai idan na mutu.
"Rubuce rubucen da 'yan soshiyal midiya suke yi a kan aure na ba zai canja komai ba, kuma ita Hajiya Jamila ta na yin kishi ne irin wanda shari'a ta yarda da shi."
Saurari tattaunawar a kasa:
A wani labarin, mun ruwaito cewar babban malamin addini, Sheikh Dahiru Bauchi ya nemi gwamnan Kano Abba Yusuf da ya mutunta umarnin kotu.
Sheikh Dahiru Bauchi na magana ne kan rigimar da ta kaure a jihar kan batun nadin sabon sarki da aka yi, wanda ya sa babbar kotun tarayya ta dakatar da nadin amma Abba bai ji ba.
Asali: Legit.ng