Home Back

Sojan Amurka za su yi bankwana da Nijar

dw.com 2024/4/28
Sojojin Amurka na aikin bayar da horo a yankin Agadez na jamhuriyar Nijar
Sojojin Amurka na aikin bayar da horo a yankin Agadez na jamhuriyar Nijar

A wata ganawa ta musamman da jakadar Amirka a Nijar Mme Kathleen Fitzgibbon ta yi da ministan cikin gidan kasar Nijar Janar Mohamed Toumba a ofishinsa ta sanar mashi da cewa, gwamnatin Amirkar na ba da kai bori ya hau game da bukatar hukumomin mulkin sojan kasar Nijar na ganin sun kwashe sojojinsu dubu da 100  da ke girke a arewacin Nijar domin mutunta matakin katse yarjejeniyar tsaron da ta hada kasashen biyu da Nijar din ta yi a cikin watan Maris na wannan shekara.

Karin Bayani: Shugaba Tchiani ya yi magana da Putin

A  jakadar Amirkar a Nijar ta ce duk da katse yarjejeniyar tsaron da ta hada kasahen biyu, Amirka a shirye take ta ci gaba da tallafa wa Nijar a karkashin hukumar raya kasashe ta Amirka ta USAID.

Kudi sama da miliyan 250 na Dalar Amirka ne gwamnatin Amirka ta zuba domin gina babbar cibiyar sojojin Amirkar da ke a Jihar Agadez, kana Amirkar za ta fice ta bar wannan sansanin soji nata ne a daidai loakcin da zaman arba tsakanin kishiyarta ta Rasha da Nijar ke kara armashi.

Yanzu ‘yan kasa sun zura ido su ga ko matakin korar sojojin Amirka ba zai shafi harkokin diplomasiyyar kasashen biyu ba a nan gaba kamar yadda ta kasance da Faransa a baya,a daidai loakcin da kasar rasha ke ci gaba da baza komarta a kasar ta Nijar da ma sauran kasashen yankin sahel.

 
People are also reading