Home Back

Tinubu ya yi ta’zaiyyar rasuwar Kabiru Yusuf

premiumtimesng.com 4 days ago
Tinubu ya yi ta’zaiyyar rasuwar Kabiru Yusuf

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya aike da ta’zaiyyar rasuwar wani gogaggen ɗan jarida, Kabir Yusuf.

Marigayi Yusuf ya rasu a jiya Talata bayan kammala aikin Hajji na bana ya koma Kano a karshen Mako.

Kafin rasuwar sa, marigayin shi ne wakilin jaridar The Triumph da Radio France a Abuja.

A sanarwar da mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale a yau Laraba, Tinubu ya taya iyali, ƴan uwa da abokan arziki na mamacin jimamin rasuwar ɗan jaridar.

People are also reading