Home Back

Kasurgumin Kwamandan Yan Bindiga Ya Mika Wuya Ga Sojoji a Kaduna

legit.ng 2024/7/1
  • Wani hatsabibin ɗan bindiga, Lawal Kwalba ya miƙa wuya ga rundunar sojojin Najeriya a jihar Kaduna ranar Talata
  • A wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar, ta ce tubabben ɗan ta'addan ya mika makamai da kayan aikinsa ga dakarun sojoji
  • Ta ce wannan wata alama ce da ke nuna hare-hare. da jami'an tsaro ke kai wa maɓoyar yan ta'adda ya matsa masu lamba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kaduna - Wani ƙasurgumin kwamandan ƴan bindiga, Lawal Kwalba ya miƙa wuya ga rundunar sojojin Nsjeriya a jihar Kaduna.

Rundunar sojojin ƙasa ta Najeriya ce ta bayyana haka a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na manhajar X wanda aka fi sani da Twitter yau Laraba.

Sojojin Najeriya.
Kwamandan yan bindiga Lawal Kwalba ya tuba ya mika wuya ga sojoji a Kaduna Hoto: Nigeria Army Asali: Twitter

Sanarwan ta ce wannan na zuwa ne yayin da dakarun sojoji ke ci gaba matsa wa ƴan ta'adda da nufin kawo karshen duk wani nau'in ta'addanci a ƙasar nan.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Rundunar ta ce kwamandan ƴan bindigan ya miƙa kansa ranar Talata 28 ga watan Mayu, 2024 biyo bayan zafafan hare-haren da sojoji ke kai wa mafakar ƴ biniga a Kaduna.

A cewar sanarwar, babu ko shakka hare-haren da sojoji ke kai wa maɓoyar ƴan ta'adda daban-daban sun hana su sakat, wanda bisa haka ne Kwalba ya zaɓi miƙa wuya.

Wani sashin sanarwar ya ce:

"Wannan miƙa wuya ya nuna irin nasarorin da sojoji ke samu a yaƙi da ƴan ta'adda a jihar Kaduna da kewaye.
"Bayan ya miƙa wuya, sojojin sun karɓi bindigogi kirar AK-47 guda biyu, babur daya, da Magazine biyu dauke da harsashi na musamman daga hannun dan ta'addan."

A halin yanzu dai Kwalba na hannun sojoji a ɗaya daga cikin sansanonin su kuma ana sa ran za a samu muhimman bayanai da zasu taimaka waje. kakkaɓe sauran ƴan ta'adda.

Rundunar sojojin ta tabbatar da cewa dakaru za su ci gaba da aiki ba dare ba rana domin dawo da zaman lafiya da tsaro a Kaduna da yankin baki ɗaya.

ISWAP ta kashe masunta a Borno

A wani rahoton kuma ƴan ta'adda ɗauke da makamai na ƙungiyar ta'addanci ta ISWAP sun kao hari kan masunta a ƙaramar hukumar Kukawa ta jihar Borno.

Miyagun ƴan ta'addan sun hallaka masunta mutum 15 lokacin da suke shirin fara kun kifi da daddare a ranar Lahadi.

Asali: Legit.ng

People are also reading