Jigon PDP ya 'Fallasa' Babban Dalilin Rikicin Nyesom Wike da Sabon Gwamnan Ribas
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Rivers-Wani jigo a jam'iyyar PDP, Dele Momodu ya bayyana dalilin barakar da ke tsakanin tsohon gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike da magajinsa Siminalayi Fubara.
A cewar Momodu, shugabannin biyu sun samu sabani kan wanda zai rika juya asusun gwamnatin Ribas ne.
A rahoton da Daily Trust ta wallafa, Dele Momodu ya ce Wike da Fubara sun fara takun saka ne tun bayan da Fubara ya dare kan mulkin jihar tare da tafyar da al'amuransa.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya zargi shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da kokarin amfani da Wike wajen shiga baitul malin jihar Rivers din.
Dele Momodu ya kara da cewa kudin jihar Rivers na taka muhimmiyar rawa wajen zaben kasar nan, shi ya sa Shugaba Tinubu ke son Wike ya rike musu jihar.
Daya daga cikin jiga-jigai a jam'iyyar PDP, Dele Momodu ya ce su na sane da yadda APC karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ke amfani da daya daga cikinsu wajen rarraba kan 'ya'yan jam'iyyar.
Dele Momodu wanda ya bayyana hakan ta cikin wata hira da Channels Television ya ce da mamaki yadda gwamnatin Tinubu ke kokarin murkushe adawa duk kuwa da yadda ya jagoranci adawa lokacin ya na gwamnan jihar Lagos.
Sai dai ya na ganin sannu a hankali za su dinke barakar, domin a cewarsa, Atiku Abubakar dan takararsu a zaben shugaban kasar da ya gabata na kokarin hada kawunan 'yan jam'iyyar.
Dele Momodu ya ce za su ba APC mamaki a zabe mai zuwa na shekarar 2027.
A baya mun kawo muku cewa gwamnan jihar Rivers, Fubara Siminalayi ya sha alwashin gudanar da al'amuran jiharsa ba tare da durkusawa wani ba.
Gwamnan ya kuma sha alwashin aiki tukuru wajen kare albarkatun jiharsa a dai-dai lokacin da su ke tsaka da dambarwa da tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike.
Asali: Legit.ng