Rikicin Masarauta: Kwankwaso Ya Bayyana Masu Son Kawo Hargitsi a Kano
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Kano - Jagoran jam'iyyar NNPP na ƙasa kuma madugun Kwankwasiyya, Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi zargin cewa maƙiya Kano na shirin ruguza jihar.
Kwankwaso wanda a baya ya taɓa zama gwamnan Kano, ya yi kira ga al’ummar jihar da su haɗa ƙarfi da ƙarfe domin samar da zaman lafiya da ci gaban jihar.
Kwankwaso ya yi wannan kiran ne a wajen bikin Sallah na musamman da gidauniyar Kwankwasiyya Development Foundation ta shirya a Kano, wanda aka gudanar a gidansa jiya Talata, cewar rahoton jaridar The Nation.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Ya ce lokaci yayi da duk ƴan asalin Kano da ƴan jam’iyyar NNPP za su haɗa kai, bisa la’akari da matsalolin da jihar ke fuskanta daga manyan ƴan siyasa daga ɓangarori daban-daban, rahoton Voice of Nigeria ya tabbatar.
Fadar shugaban ƙasa ta musanta zargin da Kwankwaso ya yi cewa gwamnatin tarayya na shirin sanya da dokar ta ɓaci a Kano kan rikicin masarautar da ake yi.
Dangane da rikicin masarautar Kano, Kwankwaso ya ce maƙiyan jihar sun mayar da abin siyasa domin adawa da dawo da ainihin yadda gidan sarautar yake a baya.
"Mun lashe zaɓe da gagarumin rinjaye amma maƙiyan jihar na ƙoƙarin ƙwacewa, amma Allah cikin ikonsa bai bar su ba."
"Alamu sun nuna kamar maƙiyan sun ƙara dawowa. Kun san abin da ke faruwa dangane da masarauta sannan muna godiya ga dukkanin masu goyon bayan gwamnati."
- Rabiu Musa Kwankwaso
A wani labarin kuma, kun ji cewa jam’iyyar APC reshen jihar Kano, ta yi kira ga hukumomin tsaro da su gaggauta cafke Rabiu Kwankwaso, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP.
Hakan na zuwa ne bayan Kwankwaso ya zargi gwamnatin tarayya ƙarƙashin jam’iyyar APC da ƙyanƙyasar sababbin ƴan ta’adda a jihar Kano.
Asali: Legit.ng