Home Back

Aliko Dangote Zai Gina Wani Sabon Kamfanin Siminti a Arewacin Najeriya

legit.ng 2024/5/17
  • Wanda ya fi kowa arziki a Afrika, Alhaji Aliko Dangote, ya yi alkawarin kafa sabon kamfanin siminti a jihar Gombe
  • Ya bayyana haka ne yayin hira da 'yan jarida jim kaɗan bayan ganawar sirri da ya yi da gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya
  • Ya kuma bayyana dalilai da suka sa ya zabi jihar Gombe domin kafa kamfanin da kuma yadda za a samu sauƙin farashin siminti da zarar ya gama aikin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Shahararren dan kasuwa kuma mai arzikin Afrika na daya, Alhaji Aliko Dangote ya yi alkawarin gina kamfanin siminti a jihar Gombe.

Dangote
Dangote ya ce kamar yadda matatar mai dinsa ta fara kawo saukar farashi, kamfanin simintin ma zai saukar da farashi. Hoto: Dangote Industries Asali: Facebook

Alhaji Aliko Dangote ya bayyana haka ne yayin bikin auren 'yar Alhaji Umaru Kwairanga a jihar Gombe.

Dalilin Dangote na kafa kamfani a Gombe

Mai taimakawa gwamnan jihar Gombe a harkar yada labarai, Isma'ila Uba Misilli ya fitar da sanarwa a shafinsa na Facebook cewa Dangote ya ce zai kafa kamfanin ne lura da yadda al'amuran kasuwanci ke bunkasa a jihar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya kara kuma da cewa gwamnan jihar ya samar da yanayi mai kyau da zai taimakawa kasuwanci wurin habaka da kuma irin yadda jihar ke da sinadarin hada siminti sosai.

Yadda Dangote zai kawo saukar farashi

Dangote ya tabbatar da cewa idan suka fara hada siminti a jihar Gombe akwai yiwuwar farashin siminti zai sauka a yankunan da su ke kewaye da Gombe.

Za a samu wannan rangwame ne saboda rage nisan jigilar simintin da za a samu.

An dawo da dokar shara a Gombe

A wani rahoton kuma, kun ji cewa gwamnatin jihar Gombe ta sanar da dokar sharar gama gari da za a rika yi duk ranar Asabar din karshen wata a fadin jihar

Dokar zata fara aiki ne a karshen watan Afrilu kuma za a rika daukan awa biyu ana gudanar da ita ba tare da barin zirga-zirgar al'umma ba

Gwamnatin ta yi kira ga daukacin al'ummar jihar da su yi iya kokari wurin bada hadin kai ga hukumomi domin tabbatar da tsaftace jihar baki daya

Asali: Legit.ng

People are also reading