Home Back

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

bbc.com 2024/7/1

Rahoto kai-tsaye

An kusa kawo ƙarshen luguden wuta da ake yi a Gaza - Netanyahu

...

Asalin hoton, Reuters

Firaiminista Benjamin Netanyahu ya ce an kusan kawo karshen luguden wutar da ake yi a birnin Rafa da ke kudancin Gaza, amma zai ci gaba da yaki da Hamas sai sai sun kauda ta daga madafun iko.

Netanyahu ya ce: "Bayan kammala wannan, za mu samu damar nausa dakarunmu zuwa arewaci, za mu yi hakan, sannan za mu dawo da mazauna yankunan arewaci da kudanci da aka kwashe, ta amfani da dabarun diflomasiyya".

A bangare guda ministan tsaron Isra'ila Yoav Gallant, ya isa birnin Washington na Amurka, domin tattaunawa kan yakin Gaza da tashin hankali tsakaninsu da kungiyar Hezbollah ta Lebanun.

People are also reading