Home Back

Hajjin Bana: Kaduna Ta Yi Jigilar Alhazai Fiye Da 1,600 Zuwa Saudiyya

leadership.ng 2024/7/3
Maniyyatan Nijeriya

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kaduna ta yi nasarar jigilar maniyyata fiye da 1,600 zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana.

Kashi na baya-bayan nan, wanda ya kunshi maniyyata 515, sun tashi ne a jiya Lahadi ta kamfanin Max Air, mai jigilar alhazan Kaduna.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Yunusa Muhammad ne ya bayyana hakan a wata sanarwa.

Ya ce, hakan ya kawo adadin maniyyata 1,612 da aka yi jigilarsu daga jihar ya zuwa yanzu.

Ya ce, a halin yanzu, an fara tantance maniyyatan da ake shirin jigila a jirgi na hudu a sansanin jigilar alhazai da ke Mando Kaduna, kuma a yau Litinin ne ake sa ran tashinsu.

People are also reading