Home Back

Mu Muka Kai Buhari Villa, Amma Ya Jefa Mu Masifar Tsadar Rayuwa Inji Mawaki Rarara

legit.ng 2024/4/29
  • Dauda Adamu Kahutu 'Rarara' ya sake bayyana illar da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya yi wa Najeriya
  • Mawaƙin siyasar ya yi nuni da cewa Buhari ne silar jefa mutanen ƙasar nan cikin halin masifar da ake ciki a yanzu
  • Ya ce dole dala ta yi tashin gwauron zabi domin Buhari ya sayar da man fetur na shekara biyu ya karɓe kuɗin kafin ya ba Bola Tinubu mulki

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Shahararren mawaƙin siyasar nan, Dauda Adamu Kahutu 'Rarara', ya sake zargin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, da jefa ƴan Najeriya cikin masifa.

Ko a baya dai Rarara ya fito ya bayyana cewa sai da Buhari ya yi tumu-tumu da ƙasar nan kafin ya miƙa ta a hannun shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Rarara ya caccaki Buhari
Rarara ya sake fadin illar da Buhari ya yi wa Najeriya Hoto: Muhammadu Buhari, Dauda Rarara Asali: Facebook

A wani faifan bidiyo da wani mai amfani da sunan @bb_khamees a shafin X (wanda a baya aka fi sani da Twitter) ya sanya, mawaƙin ya zayyano illar da Buhari ya yi wa Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wace ɓarna Rarara ya ce Buhari ya tafka?

Rarara ya bayyana cewa dole a sha wuya a Najeriya domin man da ake sayarwa a samu Dala, Buhari ya sayar da shi kafin ya sauka daga kan mulki.

Mawaƙin wanda a baya ya yi waƙokin tallata Buhari, ya ce dole ne a fito a gaya mutane gaskiya kan yadda tsohon shugaban ƙasan ya jefa ƙasar nan cikin halin ɗa ta tsinci kanta a ciki yanzu.

Kalaman Rarara game da mulkin Buhari

"Duk wannan tashin dala da wata masifa da ake ciki a Najeriya, Buhari ne ya saka mu a cikinta.
"Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari wanda mu muka ɗauke shi muka kai shi wannan gida, muka dawo da shi muka sake kai shi, shi ya sanya mu a cikin wannan bala'in."
"Ya za a yi dala ba za ta tashi ba, dalar nan ba mu da ita, man fetur muke sayarwa a ba mu dala. Man fetur na shekara biyu daga lokacin da Tinubu ya hau, Buhari ya sayar ya karɓi kuɗaɗen. Ina za a samu dalar?"

Rarara ya yi nuni da cewa dole ne fa ƴan Najeriya su ci gaba da haƙuri domin ɓarnar da aka yi sai an sha wuya kafin a gyara ta.

Rarara yana son kujerar minista

A wani labarin kuma, kun ji cewa mawaƙin siyasar nan Dauda Adamu Kahutu 'Rarara', ya bayyana cewa ya cancanci samun muƙamin minista a gwamnatin Tinubu.

Rarara ya yi nuni da cewa gudunmawar da ya bayar wajen kafuwar gwamnatin Tinubu, ta cancanci a saka masa.

Asali: Legit.ng

 
People are also reading