Kotu Ta Yi Hukunci Kan 'Yancin Dalibai Mata Musulmai Su Sanya Hijabi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
Jihar Oyo - Babbar kotun jihar Oyo, da ke Ibadan ta yanke hukuncin cewa ɗalibai mata musulmai na makarantar 'International School' ta jami'ar Ibadan, suna da damar sanya hijabi a saman kayan makarantarsu.
Alƙalin kotun mai shari’a Moshood Ishola ya ce ƴancin yin addini yana cikin kundin tsarin mulkin Najeriya.
Da yake yanke hukunci a ƙarar a ranar Laraba, alƙalin ya ce hukuncin nasa yana da nasaba da hukunce-hukuncen da Kotun Ƙoli ta yanke a baya, cewar rahoton jaridar The Nation.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Wasu ɗaliban makarantar tare da goyon bayan iyayensu, suka shigar da ƙarar hukumar gudanarwar makarantar a shekarar 2018, rahoton Daily Post ya tabbatar.
Sun haƙiƙance cewa suna da ƴancin sanya hijabi a saman kayan makarantarsu.
Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Faridah Akerele, Aaliyah Dopesi, Akhifah Dokpesi, Raheemah Akinlusi, Imam Akinoso, Hamdallah Olosunde da Aliyyah Adebayo.
Sauran su ne Moriddiyah Yekinni, Ikhlas Badiru, Mahmuda Babarinde, da Fareedah Moshood.
Alƙalin ya ce makarantar a matsayinta na ta gwamnati, ya kamata ta ba ɗalibai mata musulmi damar ƴancin sanya hijabi.
"Makarantar, malamanta, ko wakilanta ba su da hurumin hukunta ɗalibai saboda yin amfani da hijabi a harabar makarantar ko kuma wajen harabar makarantar."
- Mai shari'a Moshood Abiola
A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin ƙasar Faransa ta haramta ɗalibai sanya ɗalibai musulmai sanya hijabi a makarantun gwmanatin na ƙasar.
Gabriel Attal, ministan ilmi na ƙasar Faransa ya bayyana hijabi a matsayin wata alamar addini ce wacce take kawo barazana ga tsarin kafa makarantu kan yi wa kowane addini adalci.
Asali: Legit.ng