Aikin Hajji: Najeriya Na Shirin Kafa Asibitoci a Makkah, Ta Na Jiran Amincewar Saudiya
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida
Abuja - Hukumar alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta ce ta na jiran amincewar Saudiya domin kafa asibitoci da za su zama karkashin kulawar likitocin Najeriya da aka tura Makkah.
Hukumar ta kuma shawarci maniyyatan Najeriya da ke Makkah domin gudanar da aikin hajjin 2024 da su nemi lafiya a asibitocin kasar Saudiya.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Usara ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, kamar yadda jaridar The Cable ta ruwaito.
Yayin da take tabbatar wa alhazai cewa asibitocin Najeriya da ke Makkah na da ma’aikata da kayan aiki, Usara ta ce asibitocin ba za su iya yin aiki ba har sai Saudiya ta ba da izini.
Fatima Usara ta kara da cewa har yanzu babu wata kasa da ke halartar aikin hajjin da aka ba wa izinin kafa asibitoci a Makkah.
Ta kuma shawarci alhazai da su guji shan magani ba bisa ka'ida ba, sannan ta ja hankalin alhazan da su nemi taimako daga kungiyar likitocin Najeriya.
Jaridar Tribune ta ruwaito shugaban kwamitin likitocin NAHCON da aka tura Saudiya, Dr Abubakar Adamu Ismail ya ce an ba Najeriya damar kafa asibitoci a Madinah ban da Makkah.
A wani labarin, mun ruwaito cewa gwamnatin jihar Kebbi ta tabbatar da rasuwar daya daga cikin maniyyatan jihar da suka je Saudiyadomin gudanar da ayyukan hajjin bana.
Rasuwar Muhammad Sulaiman, ta kara adadin yawan alhazan jihar Kebbi da suka rasu a Makkah zuwa biyu, bayan mutuwar Hajiya Tawakaltu Alako.
Asali: Legit.ng