El-Rufai Ya Shirya Yin Fada da Gwamnatin Shugaba Tinubu, Bayanai Sun Fito
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi
FCT, Abuja - Nasir Ahmad El-Rufai, tsohon gwamnan jihar Kaduna yana shirin "yaƙi" da Shugaba Bola Tinubu a aƙalla kotuna biyu.
Kamar yadda jaridar Vanguard ta ruwaito a ranar Asabar, 6 ga watan Afrilu, za a gabatar da faɗan ne a kotunan Najeriya.
El-Rufai na sa ran wanke sunansa daga zargin cewa yana da hatsarin tsaro wanda ya hana shi samun muƙamin minista.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Tsohon gwamnan yana son wanke kansa ne bayan da wasu masu sharhi suka ce zai ƙalubalanci sake tsayawa takarar Shugaba Tinubu a 2027.
Rahotanni sun ce na kusa da El Rufa’i sun bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta wulaƙanta tsohon gwamnan a bainar jama’a.
Rashin samun muƙamin na El-Rufai ya ba na kusa da shi mamaki duba da irin rawar da ya taka wajen sanya gwamnonin Arewacin Najeriya suka marawa Tinubu baya a lokacin zaɓen 2023.
Jaridar Vanguard ta ambato wani na kusa da El Rufai yana cewa:
"Kuna tunanin cewa Mallam zai bari wannan tambarin ya tsaya a kansa? Ina mai tabbatar muku da cewa zai wanke sunansa a gaban kotu."
A wani labarin kuma, kun ji cewa Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa'i ya ziyarci shugabannin jam'iyyar adawa ta SDP.
Tsohon gwamnan ya kai wannan ziyarar ne yayin da ake ci gaba da raɗe-raɗin cewa yana shirin tattara ƴan komatsansa ya fice daga jam'iyyar APC mai mulki.
Asali: Legit.ng