Home Back

EFCC Na Neman Yahaya Bello Ruwa A Jallo Kan Zargin Almundahanar N80.2b

leadership.ng 2024/5/17
EFCC Na Neman Yahaya Bello Ruwa A Jallo Kan Zargin Almundahanar N80.2b

Hukumar Yaki da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC), ta fara neman Yahaya Bello ruwa a jallo kan zargin almundahanar Naira biliyan 80.2.

EFCC ta yi kira ga duk wanda ke da bayanan da za su kai ga cafke tsohon gwamnan Kogi, ya kai rahoto ga hukumar ko ‘yansanda.

Wannan na cikin wani sakon da hukumar ta wallafa a yammacin ranar Alhamis a shafinta na Facebook.

“EFCC na neman tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin badakalar Naira biliyan 80.2,” in ji EFCC.

“Duk wanda ke da bayanin inda za a same shi, ya kamata ya kai rahoto ga EFCC ko ofishin ‘yansanda mafi kusa da shi.”

People are also reading