Sanusi II: “Abin da Ya Hana Ni Zuwa Kotu Bayan Ganduje Ya Tsige Ni Daga Sarkin Kano”
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin
Jihar Kano - Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, ya bayyana ainihin dalilin da ya sa bai kalubalanci tsige shi a matsayin sarki da Abdullahi Umar Ganduje ya yi.
Mun ruwaito tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje ya tsige Sanusi II daga kujerar sarki a watan Maris din 2020 saboda yawan sabanin da suke samu.
A wata hira da jaridar The Sun a ranar Asabar, 22 ga Yuni, Sanusi II ya ce yana daya daga cikin daruruwan 'ya'yan sarki a masarautar don haka ba zai ce lallai sai shi kadai zai zama sarki ba.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Kamar yadda Sahara Reporters ta ruwaito, Sanusi ya bayyana cewa ko da a ce ya je kotu kuma kotu ta mayar da shi, ba zai iya yin aiki da gwamnatin Gwamna Ganduje ba.
Sanusi II, tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) ya bayyana cewa bai kalubalanci tsige shi ba a 2020, sai dai ya kalubalanci Ganduje kan tilasta mashi yin gudun hijira.
Da aka tambaye shi dalilin da ya sa bai kalubalanci tsige shi da tsohon Gwamna Ganduje ya yi ba, Sanusi II ya ce:
"Na gaya muku cewa ba ni da wani hakki na zama sarki, ina daya daga cikin daruruwan 'ya'yan sarki, Allah ne ya zabe ni, kuma idan Allah ya ce in bar kujerar, zan dauki kaddara."
"Mu kaddara ma na je kotu, kuma ta ba ni nasara, kana tunanin zan ji dadin aiki da gwamnatin jihar? Tun da gwamnan ya nuna ba ya so na, ko da na dawo, zai kuntata rayuwata ne kawai.
"Kuma a kan me zan je kotu? Ko da aka kawo mun takardar kora daga sarauta, an ce ina yi wa gwamnati zagon kasa, amma ba su gabatar da hujja ba, kenan dai, tsana ce kawai ta jawo haka."
Tun da fari, mun ruwaito gwamnatin jihar Kano, ta jaddada cewa har yanzu Muhammadu Sanusi II ne Sarkin Kano, duk da hukuncin da wata babbar kotu tarayya ta yi.
Kwamishinan shari’a na jihar, Haruna Isah Dederi ne ya bayyana hakan jim kadan bayan da kotu ta tabbatar da dokar rusa masarautun Kano amma ta rusa batun dawo da Sanusi II.
Asali: Legit.ng