Home Back

Shugaba Bola Tinubu Zai Yi Sauye-Sauye A Gwamnatinsa  Kwanan nan

leadership.ng 2024/8/22
Shugaba Bola Tinubu Zai Yi Sauye-Sauye A Gwamnatinsa  Kwanan nan

Lauya kuma mai sharhi kan harkokin yau da kullum, Daniel Bwala, ya sanar da cewa Shugaba Bola Tinubu zai ƙaddamar da sabuwar majalisar zartarwa cikin makonni kaɗan masu zuwa. Bwala ya yi wannan bayani ne a matsayin martani da suka daga shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, Mohammed Ali Ndume, wanda ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya ta kasa magance matsalolin tsaro kuma Shugaba Tinubu ya rufe ƙofarsa hatta wasu ministocin yana da wuya su iya samunsa balle yan majalisa.

A cikin wani rubutu mai taken “Ali Ndume, the rant of an expert in grandstanding,” Bwala ya tambayi abubuwan da Ndume ya cimma cikin shekaru 21 na mulkinsa, yana zarginsa da rashin jagoranci da kuma kasa ba da gudunmuwa sosai ga mutanen mazaɓarsa. Bwala ya yi iƙirarin cewa zargin Ndume kan Tinubu ba su da tushe, yana mai jaddada cewa wannan gwamnatin tana aiki tuƙuru don gyara matsalolin da gwamnatin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari ta bari.

Bwala ya kuma bayyana cewa tuni aka suna ƙoƙarin ministocin yanzu, kuma akwai canjin da za a yi nan ba da jimawa ba. Ya kare salon mulkin Tinubu, yana mai jaddada ƙudirin shugaban na tsige duk wani mamban majalisar zartarwa da ya gaza cika tsammanin ‘yan Nijeriya.

People are also reading